fidelitybank

Gwamnati ta rinƙa jigilar man fetur ta jirgin ƙasa gudun abun da ya faru da Jigawa – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya tuhumi gwamnatin Najeriya da ta rinƙa amfani da jigilar mai ta hanyar jirgin kasa a fadin kasar.

Atiku ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake mayar da martani ga fashewar tankar mai a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa.

Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, lamarin da ya faru a daren ranar Alhamis ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 100.

Da yake mayar da martani, Atiku ya wallafa a shafin X: “Na yi matukar bakin ciki da rahoton mutuwar mutane da dama a wata fashewar tankar mai a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa.

“Al’amarin da ya faru a Jigawa na da yawa da ya shafi fashewar tankokin mai a kasar nan.

“Lokaci ya yi da za mu binciko wasu hanyoyin, kamar layin dogo, na jigilar kayayyakin man fetur a fadin kasar nan.

“Har ila yau, yana da kyau a horar da direbobi masu ruwa da tsaki a harkar safarar kayan wuta da kuma duba ka’idar safarar albarkatun man fetur da sauran kayayyakin da ke da zafi.

“Ina fatan in bayyana alhinina ga jama’a da gwamnatin jihar Jigawa tare da neman a kawo musu dauki cikin gaggawa. Bai kamata a keɓe wata hanya ba wajen jinyar waɗanda suka ji rauni.

“Ina kuma jajanta wa iyalan da suka rasa ‘yan uwa a wannan mummunan lamari, ina kuma yi musu addu’a Allah ya basu lafiya, kuma marigayin ya sami hutu na har abada. -AA”

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp