fidelitybank

Gwamnati ta rinƙa jigilar man fetur ta jirgin ƙasa gudun abun da ya faru da Jigawa – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya tuhumi gwamnatin Najeriya da ta rinƙa amfani da jigilar mai ta hanyar jirgin kasa a fadin kasar.

Atiku ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake mayar da martani ga fashewar tankar mai a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa.

Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, lamarin da ya faru a daren ranar Alhamis ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 100.

Da yake mayar da martani, Atiku ya wallafa a shafin X: “Na yi matukar bakin ciki da rahoton mutuwar mutane da dama a wata fashewar tankar mai a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa.

“Al’amarin da ya faru a Jigawa na da yawa da ya shafi fashewar tankokin mai a kasar nan.

“Lokaci ya yi da za mu binciko wasu hanyoyin, kamar layin dogo, na jigilar kayayyakin man fetur a fadin kasar nan.

“Har ila yau, yana da kyau a horar da direbobi masu ruwa da tsaki a harkar safarar kayan wuta da kuma duba ka’idar safarar albarkatun man fetur da sauran kayayyakin da ke da zafi.

“Ina fatan in bayyana alhinina ga jama’a da gwamnatin jihar Jigawa tare da neman a kawo musu dauki cikin gaggawa. Bai kamata a keɓe wata hanya ba wajen jinyar waɗanda suka ji rauni.

“Ina kuma jajanta wa iyalan da suka rasa ‘yan uwa a wannan mummunan lamari, ina kuma yi musu addu’a Allah ya basu lafiya, kuma marigayin ya sami hutu na har abada. -AA”

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp