fidelitybank

Gwamnati ta musanta batun ƙarin kuɗin lantarki

Date:

Gwamnatin Najeriya ta musanta rahotannin da ke nuna cewa tana da aniyar ƙara kuɗin wutar lantarki cikin watanni masu zuwa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, mai bai wa shugaban Najeriya, Bola Tinubu shawara kan makamashi, Olu Arowolo Verheijen, wadda aka ruwaito tana cewa cewa “za a yi ƙarin kashi 65 na kuɗin”, ta ce an yi wa kalamanta gurguwar fassara.

Jami’ar dai ta yi wannan kalami ne a taron makamashi na Afirka da aka gudanar a birnin Dar es Salam na ƙasar Tanzaniya, inda jaridun Najeriya da dama suka wallafa batun.

Ta ce bayan ƙara kuɗin wutar na Band A a shekarar 2024, a yanzu kuɗin da ake samu daga wutar lantarkin ya na biyan kashi 65 ne cikin kuɗin da ake kashewa wurin samar da wutar, inda gwamatin ƙasar ke cigaba da biyan giɓin da ake samu.

Olu Verheijen ta kuma ce duk da dai gwamnatin ta duƙufa wajen samar da kuɗin wuta mai sauƙi nan gaba, abin da ta mayar da hankali kai a yanzu shi ne tabbatar da samar da ƙarin wutar lantarkin ga ƴan ƙasar, da tabbatar da rage ɗaukewar wutar, da kuma tabbatar da kare marasa ƙarfi.

A shekarar 2024 ne gwamnatin Najeriya ta janye wani ɓangare na tallafin lantarki da take biya, lamarin da ya haifar da hauhuwar farashin kuɗin wuta ga masu tsarin ‘Band A’ a faɗin ƙasar.

Lamarin ya janyo ƙorafi a faɗin ƙasar ganin irin halin taɓarɓarewar tattalin arziƙi da al’umma ke fuskanta.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp