fidelitybank

Gwamnati ta musanta batun ƙarin kuɗin lantarki

Date:

Gwamnatin Najeriya ta musanta rahotannin da ke nuna cewa tana da aniyar ƙara kuɗin wutar lantarki cikin watanni masu zuwa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, mai bai wa shugaban Najeriya, Bola Tinubu shawara kan makamashi, Olu Arowolo Verheijen, wadda aka ruwaito tana cewa cewa “za a yi ƙarin kashi 65 na kuɗin”, ta ce an yi wa kalamanta gurguwar fassara.

Jami’ar dai ta yi wannan kalami ne a taron makamashi na Afirka da aka gudanar a birnin Dar es Salam na ƙasar Tanzaniya, inda jaridun Najeriya da dama suka wallafa batun.

Ta ce bayan ƙara kuɗin wutar na Band A a shekarar 2024, a yanzu kuɗin da ake samu daga wutar lantarkin ya na biyan kashi 65 ne cikin kuɗin da ake kashewa wurin samar da wutar, inda gwamatin ƙasar ke cigaba da biyan giɓin da ake samu.

Olu Verheijen ta kuma ce duk da dai gwamnatin ta duƙufa wajen samar da kuɗin wuta mai sauƙi nan gaba, abin da ta mayar da hankali kai a yanzu shi ne tabbatar da samar da ƙarin wutar lantarkin ga ƴan ƙasar, da tabbatar da rage ɗaukewar wutar, da kuma tabbatar da kare marasa ƙarfi.

A shekarar 2024 ne gwamnatin Najeriya ta janye wani ɓangare na tallafin lantarki da take biya, lamarin da ya haifar da hauhuwar farashin kuɗin wuta ga masu tsarin ‘Band A’ a faɗin ƙasar.

Lamarin ya janyo ƙorafi a faɗin ƙasar ganin irin halin taɓarɓarewar tattalin arziƙi da al’umma ke fuskanta.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp