Fadar Gwamnatin Tarayya, ta yi martani kan umarnin da wani alƙali a wata kotun Amurka da ke zamanta a birnin Washigngton DC ya bayar, inda ya buƙaci a fitar da bayanan zargin Tinubu da safarar ƙwayoyi.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce wannan ba sabon ba ne.
Ya ce, “ƴan jarida suna ta neman jin ta bakin fadar shugaban Najeriya kan hukuncin alƙalin kotun Amurka da ke Washington, inda ya buƙaci FBI da DEA su fitar da sakamakon binciken da aka yi wa Bola Tinubu kan zarginsa da safarar miyagun ƙwayoyi.
“Amsarmu ita ce babu wani sabon abu a hukuncin. Sakamakon bincike ya daɗe da fita, domin rahoton binciken FBI da DEA sun fi shekara 30 a fili. Rahoton bai nuna shugaban Najeriya yana da laifi ba.”