fidelitybank

Gwamnati ta kwato bashin kudade Naira biliyan 57 daga ma’aikatu da hukumomi

Date:

Daraktar ayyuka na musamman na ma’aikatar kudi ta tarayya, Aisha Omar, ta ce kawo yanzu ma’aikatar ta kwato Naira biliyan 57 daga cikin Naira tiriliyan 5.2 daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da ake bin su ba shi.

Aisha Omar ta bayyana haka ne a yayin taron wayar da kan jama’a kan yadda gwamnatin tarayya ta bullo da shirin dawo da basussuka ta hanyar Project Lighthouse na shiyyar Kudu maso Gabas, ranar Talata a Enugu.

Yayin da take bayyana bude taron, Aisha Omar ta ce basussukan sun fito fili ne daga bayanan da aka tattara daga masu bi bashi fiye da 5,000 a cikin sama da hukumomi 93.

AishadOmar wanda mataimakiyar daraktan ayyuka ta musamman ce a ma’aikatar kudi ta Abuja, waddda Bridget Molokwu ta wakilta, ta ce basussukan sun kasance kamar bashin da ake bin hukumar tara haraji ta tarayya, FIRS.

Daraktan ta ce, an kuma samu kudaden da aka mayarwa gwamnati daga kamfanonin da suka kasa cika ayyukan da aka biya.

Sauran su ne wuraren rancen da ba a biya ba ga ƙungiyoyin kamfanoni da daidaikun mutane ta Bankin Masana’antu (BOI) da Bankin Noma, BOA, Bashin Hukunci don goyon bayan Gwamnati, basussukan da ke bin Hukumar Kula da Tsare Tsare-Tsare na Fansho (PTAD) ta kamfanonin inshora da sauransu.

Ta kara da cewa bayanai daga Project Lighthouse sun nuna cewa kamfanoni da daidaikun mutane da dama, wadanda suke bin hukumomin gwamnati basussukan da suka ki cika hakkinsu har yanzu ana biyan su.

Ta ce, an yi hakan ne ta hanyar kafafan gwamnati irin su GIFMIS da Treasury Single Account, TSA, saboda rashin hangen nesa kan wadannan hada-hadar.

A cewarta, a cikin aiwatar da burin dawo da bashi, Ma’aikatar Kudi ta Tarayya ta ƙaddamar da “Project Lighthouse”, wanda ya ba da damar tattara bayanan tattalin arziki da na kuɗi daga hukumomi da yawa waɗanda har yanzu ba su raba bayanai ba.

“Gabaɗaya, an taimaka magudanar kudaden shiga ta hanyar musayar bayanai da kuma aiwatar da su.

“Zai iya ba ku sha’awar sanin cewa Ma’aikatar ta hanyar ƙoƙarce-ƙoƙarce na Ƙoƙarin Binciken Bashi da Bayar da Rahoto, ta sami damar tara manyan basussuka na kusan Naira Tiriliyan 5.2.

“Har yanzu ana ci gaba da kokarin tara basussuka. A halin yanzu, an kwato kusan Naira biliyan 57 daga cikin wannan kudi, sakamakon hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki da gwamnatin tarayya suka yi.” Inji ta.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp