fidelitybank

Gwamnati ta kara kudin abincin Fursunoni da kaso 50

Date:

Gwamnatin Tarayya ta amince da ƙara kashi 50 na kuɗin abincin fursunonin da ke gidajen gyaran hali a faɗin ƙasar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja babban birnin ƙasar, kakakin Hukumar Gidajen Gyara Hali na ƙasar, Umar Abubakar ya ce an ƙara kuɗin abincinne la’akari da yanayin tsadar abinci da ake ciki.

Ya ce ƙarin zai fara aiki ne daga watan Agusta a wani yunƙuri na inganta rayuwar mazauna gidajen yarin.

“Kwana huɗu da suka gabata na yi wa tattaunawa a game da wani bidiyo da ake yaɗawa da ake zargin na abincin ƴan gidan yari ne. Tuni Hukumar Gidajen Gyara Hali ta kafa kwamitin bincike a kan bidiyon, sai dai ba zan yi magana sosai a kan sakamakon binciken ba.

“Amma saboda tsadar abinci, Gwamnatin Tarayya ta amince da ƙara kuɗin abincin ƴan gidan yari da kashi 50, kuma wannan karo na farko na ƙarin ne”.

Ya kuma bayyana cewa mazauna gidajen yarin da dama suna karatu a jami’o’in Najeriya, a cewarsa har da mutum shida masu karatun PhD, da kuma mutum 1,000 masu karatun digiri na farko a lokacin da suke zaune a gidajen yarin.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp