Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da wani shiri na magance mace-macen mata masu juna biyu da yara.
Ana sa ran shirin zai rage matsalar ta mace-macen mata da yara da kashi 25 nan da shekarar 2025, kuma ana sa ran zai shafi mutn miliyan 2.3.
An yi ƙiyasin cewar za a kashe kuɗi dala milliyan 4.35 wurin aiwatar da shirin, kuma ana sa ran ƙungiyar ta Rotary ce za ta bayar da tallafin.
Wani rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya ya nuna Najeriya ce ke da kashi ɗaya cikin huɗu na mace-macen mata da yara da ake samu a faɗin duniya.
Karanta Wannan: Majalisar dattijai ta amince da dokar cibiyar kiwon lafiya ta tarayya
A cewar rahoton abubuwan da suka fi yin sanadiyyar rayukan matan sun haɗa da zubar da jini bayan haihuwa, da cutar jijjiga da kuma matsalolin da ake fuskanta lokacin zubar da ciki.
Sai kuma gudawa da malariya waɗanda ke sanadin mutuwar yara da dama.