fidelitybank

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Date:

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan Comfort Emmanson, fasinjar nan da ake zargi da tayar da hankali a cikin jirgin Ibom Air.

Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo ne ya sanar da hakan a ranar Laraba bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar jiragen sama.

Ministan ya ce an yanke wannan hukunci ne bayan duba lamarin da jin kiraye-kirayen wasu manyan mutane, da kuma la’akari da nadamar da wadanda abin ya shafa suka nuna.

Kamfanin Ibom Air ya amince ya janye ƙorafinsa kan matar, wadda aka tsare kan lamarin da ya faru ranar 10 ga watan Agusta inda aka zarge ta marin ma’aikaciyar jirgin da kuma yin rikici da jami’an kula da filin jirgin sama.

“A lokacin da ‘yansanda suka ɗauki bayaninta a gaban lauyanta, ta nuna nadama sosai kan abin da ta aikata,” in ji ministan.

Bidiyon da ya naɗi tirka-tirkar ya karaɗe shafukan sada zumunta, inda ‘yan Najeriya da dama suka dinga sukar jam’ian tsaron ƙasar da kuma kamfanin jirgin na Ibom Air game da yadda aka fitar da matar da ƙarfin tsiya daga cikinjirgi, lamarin da ya jawo aka yi mata tsirara.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp