fidelitybank

Gwamnati ta haramta masu Otal su rinƙa baiwa ƙananan yara Mata ɗaki

Date:

Ma’aikatar mata ta ce, za ta hana dukannin otal-otal na ƙasar nan bai wa ‘yan mata masu ƙananan shekaru ɗakuna.

Ministar al’amuran mata ta ƙasa, Uju Kennedy-Ohaneye ce ta bayyana hakan, a lokacin da take jawabi a wajen wani taron buɗe horaswa da bayar da tallafi a Abuja.

Mrs Kennedy ta ce, matakin ya zama wajibi a yunƙurin da ma’aikatarta ke yi don magance matsalar safarar bil’adama a ƙasar.

Ministar na mayar da martani ne game da wata yarinya ‘yar Najeriya da aka kuɓutar a Ghana bayan da aka yi zargin an yi safararta zuwa ƙasar domin sana’ar karuwanci.

Ta ƙara da cewa hukumarta ta shirya tsaf! domin fara yaƙi da matsalolin safarar mutane daga gobe Litinin.

Haka kuma ministar ta umarci masu makarantu a faɗin ƙasar su ɗauki mataki kan cin zarafin da ake yi wa malamai da kuma ɗalibai da ake samu a wasu makarantun ƙasar.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp