fidelitybank

Gwamnati ta hana kamfanonin sufurin waje taba kudadensu a Najeriya

Date:

Najeriya ta hana kamfanonin sufurin jiragen sama na ƙasashen waje taɓa kuɗaɗensu da suka kai dala miliyan 450, a cewar wani jami’in ƙungiyar sufurin jirage ta duniya.

Kamfanin labarai na Reuters ya ruwaito cewa, hukumomin Najeriya, ƙasar da ta fi saura girman tattalin arziki a Afirka, sun dakatar da fitar da kuɗaɗen ƙasar waje don sayo kaya da kuma na masu zuba jarin da ke son kai wa ƙasashensu na asali.

Gwamnati ta ɗauki matakin ne saboda ƙarancin kuɗaɗen ƙasar waje da ƙasar ke fuskanta, musamman na dalar Amurka.

Mataimakin shugaban ƙungiyar ƙasa da ƙasa ta masu sufurin jiragen sama reshen Afirka da Gabas ta Tsakiya (IATA), Kamal Al Awadhi, ya ce suna yin tattaunawa da gwamnatin Najeriya “mai matuƙar wuya”. In ji BBC.

“Mun yi ta kawar da kai da fatan za a sasanta kuma hakan ba zai haifar wa ƙasar matsala ba,” kamar yadda ya faɗa wa manema labarai a birnin Doha na Qatar ranar Lahadi.

IATA ta ce ƙasashen Afirka sun riƙe wa mambobinta jumillar kuɗin da ya kai dala biliyan ɗaya, inda na Najeriya ya fi sauran yawa.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp