Gwamnatin Tarayya ta kira wani taron gaggawa da shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta NLC da takwarorinsu na TUC, a wani yunkuri na shawo kan shirin tsunduma yajin aiki da ƙungiyoyin suka shirya farawa daga ranar 3 ga watan Oktoba.
Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa, an shirya yin zaman ne da yammacin nan a fadar shugaban ƙasa da ke Aso Villa.
Tun da farko, an bayyana cewa za a yi taron ne da mislain karfe 12 na ranar Juma’a, sai dai daga baya aka ɗage shi zuwa yammaci, domin bai wa ƙungiyar ta ƙwadago damar sanar da mambobinta da ke wajen Abuja.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa NLC da TUC sun samu takardar gayyatan ne a safiyar nan ta hannun ma’aikatar ƙwadago da ayyuka.