fidelitybank

Gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki kan ƙarancin kuɗi da ake fuskanta – Ƙungiya Ƙwadago

Date:

Kungiyar Kwadago ta (NLC), ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin gaggawa wajen magance matsalar karancin kudi da ake fuskanta a kasar.

Shugaban NLC, Mista Joe Ajaero, yayi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da ya rattaba hannu tare da Mista Emmanuel Ugboaja, Sakatare Janar na NLC, a ranar Alhamis a Abuja.

Sanarwar ta fito ne a karshen taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) da aka gudanar a Owerri.

A cewar Ajaero, NEC ta nuna damuwarta kan yadda karancin kudi ya ci gaba da zama babbar matsala, inda tace hakan yana kara jefa al’umma cikin matsalolin rayuwa.

Ya ce NEC ta lura cewa ‘yan Najeriya na tilastawa su sadaukar da kashi biyar cikin dari na kudaden su kowanne lokaci da suke tura kudi, wani hali da ba za a yarda da shi ba wanda ke kara tsananta matsalolin tattalin arziki da miliyoyin mutane ke fuskanta.

“Tasirin wannan ga kananan ‘yan kasuwa da sauran masu aiki a tattalin arzikin zamani yana da matukar girma, domin wannan yanayi na kara jefa talakawa da ma’aikata cikin babban kalubale,”

“NLC na neman gaggawar shigar gwamnatin don gyara wannan gazawar tsarin da kuma kare hakkin kudi na ‘yan kasa.

“Muna sa ran Gwamnan Babban Bankin Najeriya zai dauki matakai don tabbatar da cewa kudi suna samuwa ga jama’a don gudanar da harkokin kasuwancin su,” in ji shi.

Shugaban NLC ya kuma nemi a dakatar da kudirin haraji da ke gaban Majalisar Dokokin kasa domin samun tattaunawa da fahimtar juna mai ma’ana tare da ma’aikatan Najeriya.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp