fidelitybank

Gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki kan ƙarancin kuɗi da ake fuskanta – Ƙungiya Ƙwadago

Date:

Kungiyar Kwadago ta (NLC), ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin gaggawa wajen magance matsalar karancin kudi da ake fuskanta a kasar.

Shugaban NLC, Mista Joe Ajaero, yayi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da ya rattaba hannu tare da Mista Emmanuel Ugboaja, Sakatare Janar na NLC, a ranar Alhamis a Abuja.

Sanarwar ta fito ne a karshen taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) da aka gudanar a Owerri.

A cewar Ajaero, NEC ta nuna damuwarta kan yadda karancin kudi ya ci gaba da zama babbar matsala, inda tace hakan yana kara jefa al’umma cikin matsalolin rayuwa.

Ya ce NEC ta lura cewa ‘yan Najeriya na tilastawa su sadaukar da kashi biyar cikin dari na kudaden su kowanne lokaci da suke tura kudi, wani hali da ba za a yarda da shi ba wanda ke kara tsananta matsalolin tattalin arziki da miliyoyin mutane ke fuskanta.

“Tasirin wannan ga kananan ‘yan kasuwa da sauran masu aiki a tattalin arzikin zamani yana da matukar girma, domin wannan yanayi na kara jefa talakawa da ma’aikata cikin babban kalubale,”

“NLC na neman gaggawar shigar gwamnatin don gyara wannan gazawar tsarin da kuma kare hakkin kudi na ‘yan kasa.

“Muna sa ran Gwamnan Babban Bankin Najeriya zai dauki matakai don tabbatar da cewa kudi suna samuwa ga jama’a don gudanar da harkokin kasuwancin su,” in ji shi.

Shugaban NLC ya kuma nemi a dakatar da kudirin haraji da ke gaban Majalisar Dokokin kasa domin samun tattaunawa da fahimtar juna mai ma’ana tare da ma’aikatan Najeriya.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp