Rahotanni na cewa, gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da tsarin nan na ‘babu aiki, babu albashi’, kan malaman jami’o’in da ke yajin aiki.
Idan ba a manta ba, kungiyar malaman jami’a ta ƙasa ASUU, ta tsunduma yajin aikin mako hudu a ranar 14 ga watan Fabrairu, wanda ta sabunta bayan ya kare.
Jaridar Vanguard ta ce, shugaban kungiyar National Association of Academic Technologists Comrade Ibeji Nwokoma, ta malaman jami’a ya tabbatar cewa ba a biya mambobin kungiyar albashinsu na watan Maris ba.
Sai dai Nwokoma ya ce, wannan matakin na gwamnati ba zai hana su neman hakkokinsu ba.