Gwamnatin tarayya ta ce, ta fara biyan Jami’an ‘yan sandan sabon tsarin albashin da ya ce tare da gyara musu shi.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar ranar Alhamis a shafinta na Tuwita.
Tun a cikin watan Nuwambar 2020 ne gwamnatin kasar ta yi alkawarin inganta tsarin albashin jami’an ‘yan sandan kasar.
Dama dai ‘yan kasar da dama, da ma su kansu ‘yan sandan sun sha korafe-korafen cewa albashin da gwamnatin kasar ke biyansu ya yi kadan.