Majalisar ba da shawarwari tsakanin jamâiyyu, IPAC, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dauki matakan gaggawa don tabbatar da hanyoyin lafiya da kuma fitar da wasu hanyoyi na isar da kayayyakin man fetur masu zafi.
Majalisar ta bayyana haka ne a lokacin da take maida martani kan fashewar wata tankar mai a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa, inda sama da mutane 150 suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta IPAC ta fitar dauke da sa hannun shugabanta na kasa Yusuf Mamman Dantalle, ta ce ta yi matukar bakin ciki tare da nuna alhini ga iyalan da suka rasa âyan uwansu a wannan mummunar fashewar, inda ya kara da cewa âmaganar bata isa a huce bakin ciki ba.
Majalisar ta yi nuni da cewa, a âyan kwanakin nan, alâummar kasar sun sha fama da hadurran tankokin mai da kuma fashe-fashe da suka yi sanadin mutuwar daruruwan mutane, akasari wadanda ke kwashe mai.
âRayuwar kowane alâamuran Najeriya kuma dole ne a kiyaye shi. âYan kasar su ma su daina diban mai a wuraren da hatsarin ya faru,â in ji majalisar.
âYa kamata hukumar kiyaye hadurra ta wayar da kan jamaâa game da illolin da ke tattare da irin wadannan ayyuka.
âIPAC tana goyon bayan gwamnati da alâummar jihar Jigawa a wannan lokaci na gwaji. Tare, za mu sa Nijeriya ta kasance mafi aminci, mafi kyau, da kuma girma ga ‘yan Ĉasa,” in ji ta.
Majalisar ta yi adduâar Allah Taâala ya yi wa iyalan da suka rasa âyan uwansu jaje, ya kuma ba su karfin gwuiwa wajen jure asara mara misaltuwa da samun sauki ga wadanda suka jikkata.