Ƙungiyar manyan malaman jami’o’i, (SSANU), ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin ma’aikatar ilimin ƙasar na taƙaita shekarun rubuta jarrabawar kammala sakandire a ƙasar.
A baya-baya nan ne ministan Ilimin ƙasar, Farfesa Tahir Mamman ya ce babu yaron da za a sake bari ya rubuta jarrabawar kammala sakandire ba tare da ya cika shekara 18 da haihuwa ba.
Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta umarci hukumomin shirya jarrabawar kammala sakandire na WAEC da NECO su sanya dokar cikin sharuɗansu na yi wa ɗalibai rajista.
To sai ƙungiyar SSANU ta bayyana matakin da koma-baya tare da haifar wa ɗalibai da iyayensu wasu sabbin matsaloli.
Yayin da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron ƙungiyar a Abuja, shugaban SSANU, Mohammed Ibrahim, ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta janye matakin tare da sake tuntuɓar masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi domin kauce wa haifar da matsaloli a fannin ilimin ƙasar.
Tun bayan sanar da sabon matakin ne dai, yake shan suka daga mutane da ƙungiyoyi da dama, a ƙasar, ciki har da jagoran adawar ƙasar Atiku Abubakar, wanda ya ce matakin zai daƙushe ɗalibai masu hazaƙa da fikira.