fidelitybank

Gwamnati ta dakatar da shirin kayyade shekaru a zana jarabar sakandire – SSANU

Date:

Ƙungiyar manyan malaman jami’o’i, (SSANU), ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin ma’aikatar ilimin ƙasar na taƙaita shekarun rubuta jarrabawar kammala sakandire a ƙasar.

A baya-baya nan ne ministan Ilimin ƙasar, Farfesa Tahir Mamman ya ce babu yaron da za a sake bari ya rubuta jarrabawar kammala sakandire ba tare da ya cika shekara 18 da haihuwa ba.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta umarci hukumomin shirya jarrabawar kammala sakandire na WAEC da NECO su sanya dokar cikin sharuɗansu na yi wa ɗalibai rajista.

To sai ƙungiyar SSANU ta bayyana matakin da koma-baya tare da haifar wa ɗalibai da iyayensu wasu sabbin matsaloli.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron ƙungiyar a Abuja, shugaban SSANU, Mohammed Ibrahim, ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta janye matakin tare da sake tuntuɓar masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi domin kauce wa haifar da matsaloli a fannin ilimin ƙasar.

Tun bayan sanar da sabon matakin ne dai, yake shan suka daga mutane da ƙungiyoyi da dama, a ƙasar, ciki har da jagoran adawar ƙasar Atiku Abubakar, wanda ya ce matakin zai daƙushe ɗalibai masu hazaƙa da fikira.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp