fidelitybank

Gwamnati ta dakatar da shirin kayyade shekaru a zana jarabar sakandire – SSANU

Date:

Ƙungiyar manyan malaman jami’o’i, (SSANU), ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin ma’aikatar ilimin ƙasar na taƙaita shekarun rubuta jarrabawar kammala sakandire a ƙasar.

A baya-baya nan ne ministan Ilimin ƙasar, Farfesa Tahir Mamman ya ce babu yaron da za a sake bari ya rubuta jarrabawar kammala sakandire ba tare da ya cika shekara 18 da haihuwa ba.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta umarci hukumomin shirya jarrabawar kammala sakandire na WAEC da NECO su sanya dokar cikin sharuɗansu na yi wa ɗalibai rajista.

To sai ƙungiyar SSANU ta bayyana matakin da koma-baya tare da haifar wa ɗalibai da iyayensu wasu sabbin matsaloli.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron ƙungiyar a Abuja, shugaban SSANU, Mohammed Ibrahim, ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta janye matakin tare da sake tuntuɓar masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi domin kauce wa haifar da matsaloli a fannin ilimin ƙasar.

Tun bayan sanar da sabon matakin ne dai, yake shan suka daga mutane da ƙungiyoyi da dama, a ƙasar, ciki har da jagoran adawar ƙasar Atiku Abubakar, wanda ya ce matakin zai daƙushe ɗalibai masu hazaƙa da fikira.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp