fidelitybank

Gwamnati ta ci tarar Trust TV Naira miliyan 5

Date:

Hukumar da ke sa ido kan kafafen yaɗa lbarai ta ƙasa, NBC, ta ci tarar Trust Television Network (Trust TV) naira miliyan biyar, saboda labarin da suka wallafa kan hare-haren da ake kai wa a jihar Zamfara mai taken “Nigeria’s Banditry: The Inside Story”.

Wata sanarwa da kamfanin Media Trust ya fitar ta ce, hukumar a wata takarda dauke da sa hannun darakta janar dinta, Balarabe Shehu Illela, ta ce, ta ci tarar Trust TV ne saboda ta yaɗa rahoto na musamman da ya saba ka’idojin wasu sassan ayoyin dokar hukumar.

Sai dai kamfanin Media Trsut ya ce, “Yayin da muke ci gaba da nazari kan matakin hukumar da kuma duba zabukan da muke da su, muna sanar da cewa a matsayinmu na gidan talabijin, mun yi amannar cewa, muna aiki ne, domin al’umma ta hanyar karin haske kan batun garkuwa da mutane mai sarkakiya da kuma yadda yake shafar miliyoyin jama’ar kasarmu.”

Sanarwar ta kara da cewa, rahoton ya bi salsalar zaman dar-dar a tsakanin al’umma da kuma abubuwan da suka sanya rikicin da ya sa wasu ke daukar makamai da ke jefa mutane cikin gagarumin halin kaka-na-ka-yi.

Ta ce, rahoton ya fito da matsalolin rashin adalci da kabilanci da rashin iya gudanar da mulki wadanda su ne ke haddasa irin wannan rikici.

Kazalika ya bayar da shawara kan yadda za a magance matsalolin ta hanyar tattaunawa da masana da masu ruwa da tsaki, ciki har da Ministan Yada Labarai, Alhaji Lai Mohammed, da Sanata Saidu Mohammed Dansadau, da Farfesa Abubakar Saddique na Jami’ar Ahmadu Bello, da sauransu.

A makon jiya ne gwamnatin Najeriya ta yi tur da matakin da BBC da kuma Trust TV suka dauka na yaɗa rahoton na musamman, tana mai cewa za ta dauki mataki a kansu.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp