Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, Nnamdi Kanu, ya bukaci gwamnatin Najeriya ta biya shi diyyar Naira biliyan 25.
Kanu ya bukaci wata babbar kotun tarayya da ke zama a Umuahia, jihar Abia, da ta tilastawa gwamnatin tarayya da ta biya shi diyyar Naira biliyan 25 kan kama shi da kuma dawo da shi daga Kenya.
Ya bayyana cewa, kudaden diyya ne na da sauran barnar da ya sha a sakamakon take masa hakkinsa.
Ikrarin shugaban na IPOB na kunshe ne a cikin karar da lauyansa na musamman, Aloy Ejimakor ya shigar a gaban Kotu, inda ya jaddada cewa, kama shi da aka yi a Kenya ya sabawa doka.
Ejimakor ya bayyana cewa zai jagoranci wata kungiyar lauyoyi domin neman kotun da mai shari’a Evelyn Anyadike ke jagoranta ta aiwatar da muhimman hakkokin Kanu.