Gwamnatin tarayya ta bayar da hutun aiki a ranar Laraba 25 da Alhamis 26 ga watan Disamban 2024 domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da babban sakatariyar ma’aikatan, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.
Tunji-Ojo ya miƙa gaisuwarsa ga ƴan Najeriya, sannan ya yi kira gare su yi amfani da lokacin bukuwan domin nuna ƙauna da kira ga zaman lafiya.
Ya ce gwamnatin Najeriya a shirye take ta cigaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban ƙasar, sannan ya taya kiristoci murna, tare da musu fatan alheri.