fidelitybank

Gwamnati ta bankaɗo bashin Tiriliyan 5.2 da take bin ma’aikatu da hukumomi 10 – Ministan Kuɗi

Date:

Gwamnatin tarayya na bin Ma’aikatu 10, da wasu hukumomi bashin Naira Tiriliyan 5.2, Ministar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare ta Kasa, Zainab Ahmed ta bayyana hakan.

Da take bayyana hakan jiya a wajen kaddamar da wani shiri na tantance basussuka da bayar da rahoto a jiya, a Abuja, ministan ta yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya ta kwato naira biliyan 53.5 daga sama da hukumomin basussuka 5,000 da aka bazu a sama da MDA 10 a cikin 12 zuwa 18 da suka wuce.

Ta ce, “Bayan fitowar daftarin kudi, ma’aikatar, ta hanyar karfafa aikin, ta samu damar tara manyan basussuka na kusan naira tiriliyan 5.2. Waɗannan basussukan sun fito fili daga bayanan da aka tattara daga masu bi bashi sama da 5,000 a cikin MDAs 10. Aiki tare da ofishin Akanta Janar na Tarayya (OAGF), mun samu nasarar kwato zunzurutun kudi har Naira biliyan 53.5 a cikin watanni 12 zuwa 18 da suka wuce, ta hannun Hukumar Integrated Financial Management Information System (GIFMIS)“.

Ta kara da cewa, domin karfafa kokarin aikin, an tsara takardar neman karbo basussuka, wanda sabon sashin dawo da basussuka zai sa ido.

Zainab Ahmed ta lura cewa, duk da yadda ake amfani da fasahar kere-kere a duniya mai cike da bayanai, gwamnati ba ta da al’adar yin amfani da bayanai don jagorantar tsarawa, aiwatarwa da tantance tasirin tsare-tsare da manufofinta ko ma wajen aiwatar da muhimman ayyuka.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp