fidelitybank

Gwamnati ta bankaɗo bashin Tiriliyan 5.2 da take bin ma’aikatu da hukumomi 10 – Ministan Kuɗi

Date:

Gwamnatin tarayya na bin Ma’aikatu 10, da wasu hukumomi bashin Naira Tiriliyan 5.2, Ministar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare ta Kasa, Zainab Ahmed ta bayyana hakan.

Da take bayyana hakan jiya a wajen kaddamar da wani shiri na tantance basussuka da bayar da rahoto a jiya, a Abuja, ministan ta yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya ta kwato naira biliyan 53.5 daga sama da hukumomin basussuka 5,000 da aka bazu a sama da MDA 10 a cikin 12 zuwa 18 da suka wuce.

Ta ce, “Bayan fitowar daftarin kudi, ma’aikatar, ta hanyar karfafa aikin, ta samu damar tara manyan basussuka na kusan naira tiriliyan 5.2. Waɗannan basussukan sun fito fili daga bayanan da aka tattara daga masu bi bashi sama da 5,000 a cikin MDAs 10. Aiki tare da ofishin Akanta Janar na Tarayya (OAGF), mun samu nasarar kwato zunzurutun kudi har Naira biliyan 53.5 a cikin watanni 12 zuwa 18 da suka wuce, ta hannun Hukumar Integrated Financial Management Information System (GIFMIS)“.

Ta kara da cewa, domin karfafa kokarin aikin, an tsara takardar neman karbo basussuka, wanda sabon sashin dawo da basussuka zai sa ido.

Zainab Ahmed ta lura cewa, duk da yadda ake amfani da fasahar kere-kere a duniya mai cike da bayanai, gwamnati ba ta da al’adar yin amfani da bayanai don jagorantar tsarawa, aiwatarwa da tantance tasirin tsare-tsare da manufofinta ko ma wajen aiwatar da muhimman ayyuka.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp