fidelitybank

Gwamnati ta baiwa ƴan kasuwa wa’adin wata guda su sauke farashi

Date:

Hukumar kare haƙƙin masu saye ta ƙasa (FCCPC), ta bai wa ‘yan kasuwa a faɗin Najeriya wa’adin wata guda don saukar da farashin kayayyaki da kuma daina tsawwala wa masu saye.

Sanarwar ta fito ne daga bakin sabon mataimakin shugaban hukumar, Mista Tunji Bello, a yayin wani taron kwana ɗaya da masu ruwa da tsaki suka gudanar kan tsawwala farashin kayyayaki a Abuja.

Bello ya jaddada cewa hukumar ta ɗauki matakin ne da nufin magance yawaitar tsadar kayayyaki da ke addabar masu saye a faɗin ƙasar.

Ya yi nuni da cewa, yayin da hukumar ta fahimci ƙalubalen da ‘yan kasuwa ke fuskanta, akwai damuwa kan yadda ƴan kasuwar suka ƙara farashin kayayyaki da gangan da kuma ƙoƙarin haɗa kai tsakaninsu domin cin gajiyar masu saye.

“Akwai gungun ‘yan kasuwa da ke haɗa baki da kai wajen tsawwala wa masu saye” in ji Bello, inda ya buƙaci ƴan kasuwar su yi aiki da kishin ƙasa da adalci.

Hukumar ta FCCPC ta yi amfani da sashe na 155 na dokokin kasuwanci don jaddada muhimmancin matsayar ta a kan farashin riba.

A ƙarƙashin wannan sashe, mutane ko ƙungiyoyin kamfanoni da aka samu da laifin ƙara farashin kayayyaki da gangan za su fuskanci hukunci mai tsanani, gami da tara da kuma ɗauri

Bello ya yi gargadin cewa Hukumar ta shirya tsaf domin ɗaukar tsauraran matakan tsaro a kan wadanda suka keta dokar da zarar wa’adin ya ƙare.

Bello ya bukaci masu ruwa da tsaki da ƴan kasuwa da su ba su haɗin kai, tare da karfafa musu gwiwa kan su rage farashin kayayyakinsu a cikin wata guda.

Hukumar ta FCCPC ta bayyana ƙarara cewa za ta sa ido sosai kan yadda ake bin doka da oda na kasuwanci tare da fara aiwatar da dokar a kan waɗanda ke ci gaba da tsawwala wa masu saye.

Hukumar ta mayar da hankali ne wajen tabbatar da cewa farashin ya yi daidai da kuma yadda kasuwar ke tafiya yadda ya kamata domin kare muradun masu saye da Najeriya gaba ɗaya.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp