Shugaban kwamitin majalisar wakilai kan cutar HIV, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, Amobi Godwin Ogah, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kafa dokar ta-baci dangane da cutar zazzabin cizon sauro sakamakon mummunar illar da take yi wa ‘yan kasa.
Ogah, mai wakiltar mazabar Isuikwuato/Umunneochi na jihar Abia, ya ce ya buƙaci hakan ne duba da irin barazanar da zazzabin cizon sauro ke yi wa al’umma, ya zama dole a mayar da hankali wajen kawar da sauro, wanda shi ne ya fi kashe mutane a duniya.
Ya kara da cewa kwamitin majalisar na sane da kalubalen da ake fuskanta wajen yakar wadannan cututtuka kuma za su hada kai da masu ruwa da tsaki domin ganin an yi amfani da kudaden da aka ware yadda ya kamata.
Ogah kuma ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su kara kaimi wajen kawar da sauro.