Gwamnatin tarayya ta amince kamfanin sufurin jirgin sama na Emirates na Dubai su koma gudanar da jigila a kasar nan.
Sanarwa dauke da sa hannun shugaban hukumar kula da sufurin jirgin sama ta Najeriya (NCAA), Kaftin Musa Nuhu, ta kuma aikewa da shugaban hukumar sufurin jirgin sama ta Hadaddiyar Daular Larabawa, Saif Mohammed Al Suwaid.
A wasikar, hukumar ta Najeriya ta ce, bayan nazarin da hukumomin da abin ya shafa suka dauka a kan dokokin kariya na korona da hukumomin na Dubai suka gindaya, a yanzu Najeriya ta amince, daga yanzu za su iya fara gudanar da jigilar.
Jirgin na Dubai suna zuwa Najeriya sau 21 a mako guda, yayin da Air Peace na Najeriya ke zuwa can sau bakwai a sati. Wanda tuni shima kamfanin jirgin Air Peace da ke Najeriyar shi ma ya ce zai koma jigilarsa zuwa Dubai, daga ranar 1 ga watan Maris na 2022.