fidelitybank

Gwamnati ta amince da naira tiriliyan 1.9 don aikin gyara hanyoyi 44

Date:

Majalisar zartaswa ta tarayya a ranar Laraba, ta amince da shawarar da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta bayar na ganin kamfanin mai na ƙasa NNPC ya zuba kuɗi naira tiriliyan 1.9 don aikin sake gyara hanyoyi 44 a faɗin kasa.

Mataimaki na musamman kan harkokin ƴaɗa labaru a ofishin mataimakin shugaban ƙasa, Laolu Akande, shi ya sanar da haka bayan taron da mataimakin shugaban ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta.

Akande ya ce kudaden da ake sa ran kashewa sun kasance don ci gaba da aiwatar da tsarin bunkasa ababen more rayuwa ne na tituna da kuma gyara tsarin ba da harajin zuba jari na gwamnatin tarayya, kashi na biyu na NNPC Ltd da sauran rassansa.

Ya ce majalisar ta kuma amince da masu ba da kwangilar gina tituna guda tara a ƙarkashin tsarin gwaji na shirin bunƙasa manyan tituna da gudanar da ayyukansu bayan bayar da cikakken takardar shaidar bin ka’idojin kasuwanci da hukumar kula da hanyoyin samar da ababen more rayuwa ta yi na tsawon shekaru 25.

Aikin hanyoyi da aka amince a matakin farko sun hada da hanyar Benin-Asaba da Abuja-Lokoja-Onitsha-Owerri-Aba-Shagamu-a Benin da Abuja-Keffi-Akwanga-Lafia da Makurdi da hanyar Kano-Maiduguri da hanyar Enugu-Port Harcourt da Legas-Ota-Abeokuta da kuma Legas-Badagry zuwa Seme.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp