fidelitybank

Gwamnati ta ƙara kuɗin Fasfon tafiye-tafiyen ƙasashen waje

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ƙara kuɗin mallakar fasfon tafiye-tafiyen ƙasashen waje, wanda sabon ƙarin zai fara aiki daga ranar ɗaya ga watan Satumban 2024.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar shige da fice ta ƙasar, DCI Kenneth Udo ya fitar, ya ce ƙarin na cikin yunƙurin gwamnatin na tabbatar da ingancin fasfo na ƙasar.

Ya ce daga wannan ƙarin, fasfo mai shafi 32 wanda yake yin shekara 5, wanda a baya ake yin sa kan naira 35,000, yanzu ya koma naira 50,000; sannan fasfo mai shafi 64, mai wa’adin shekara 10, wanda a baya ake samun sa a kan naira 70,000, yanzu ya koma Naira 100,000.

Sai dai sanarwar ta ƙara da cewa ba a ƙara kuɗin na fasfo ba ga ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje.

Da take bayar da haƙuri a kan matakin, da kuma damuwar da lamarin zai iya haifarwa, hukumar ta tabbatar wa ƴan Najeriya cewa a shirye take da cigaba da yin aiki tuƙuru domin yin abin da ya dace.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp