fidelitybank

Gwamnati na za ta ci gaba da yin adalci ga duk wani addini a jihar Oyo – Makinde

Date:

Gwamna Seyi Makinde, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da yin adalci ga duk wani addini a jihar Oyo.

Makinde ya bayyana haka ne a ranar Lahadin da ta gabata a birnin Ibadan, yayin wani gagarumin gangami da kungiyar matasan Musulmi ta kasa (NACOMYO), reshen Oyo, ta shirya, domin murnar shiga sabuwar shekara ta Musulunci, 1444H.

An gudanar da taron ne a filin wasa na Obafemi Awolowo dake Ibadan. A cewar People Gazette.

Gwamnan wanda mataimakin gwamna Adebayo Lawal ya wakilta, ya ce, gwamnatinsa ta kasance ta na kiyaye daidaiton addini.

A cewarsa, Musulmai 9 na daga cikin mambobi 17 a majalisar zartarwa ta jihar, yayin da sauran takwas kuma Kiristoci ne.

Ya kuma yi kira ga malaman addinin Musulunci da su ci gaba da yi wa gwamnatinsa addu’a domin samun nasara.

Gwamnan, a wajen taron, ya bayyana bayar da gudunmawar Naira miliyan 2.5 domin tallafa wa NACOMYO.

Ko’odinetan NACOMYO a jihar, Dawood Afolabi, ya yabawa gwamnatin Mista Makinde bisa ayyana ranar hutu domin murnar zagayowar ranar farko ta sabuwar shekarar Musulunci.

Afolabi ya ce, gwamnan ya dade yana magance koke-koken al’ummar Musulmi game da nade-naden mukamai da aka yi a gwamnatinsa.

Ya kuma ba wa Makinde tabbacin goyon bayan musulmin jihar “muddin kun tabbatar da adalci na addini a kowane fanni na mulki.”

Lakca mai taken ‘Zaben 2023: Musulmai da kuma tasirin rinjaye na adalci’, ya kasance wanda Afeez Oladosu ya gabatar yayin taron.

Oladosu ya bukaci Musulmin Oyo da su yi rajista tare da karbar katin zabe na dindindin (PVC) gabanin babban zabe na 2023.

Ya kuma bukaci masu zabe da su zabi shugabanni masu tsoron Allah cikin hikima a lokacin zaben.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp