Gwamna Seyi Makinde, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da yin adalci ga duk wani addini a jihar Oyo.
Makinde ya bayyana haka ne a ranar Lahadin da ta gabata a birnin Ibadan, yayin wani gagarumin gangami da kungiyar matasan Musulmi ta kasa (NACOMYO), reshen Oyo, ta shirya, domin murnar shiga sabuwar shekara ta Musulunci, 1444H.
An gudanar da taron ne a filin wasa na Obafemi Awolowo dake Ibadan. A cewar People Gazette.
Gwamnan wanda mataimakin gwamna Adebayo Lawal ya wakilta, ya ce, gwamnatinsa ta kasance ta na kiyaye daidaiton addini.
A cewarsa, Musulmai 9 na daga cikin mambobi 17 a majalisar zartarwa ta jihar, yayin da sauran takwas kuma Kiristoci ne.
Ya kuma yi kira ga malaman addinin Musulunci da su ci gaba da yi wa gwamnatinsa addu’a domin samun nasara.
Gwamnan, a wajen taron, ya bayyana bayar da gudunmawar Naira miliyan 2.5 domin tallafa wa NACOMYO.
Ko’odinetan NACOMYO a jihar, Dawood Afolabi, ya yabawa gwamnatin Mista Makinde bisa ayyana ranar hutu domin murnar zagayowar ranar farko ta sabuwar shekarar Musulunci.
Afolabi ya ce, gwamnan ya dade yana magance koke-koken al’ummar Musulmi game da nade-naden mukamai da aka yi a gwamnatinsa.
Ya kuma ba wa Makinde tabbacin goyon bayan musulmin jihar “muddin kun tabbatar da adalci na addini a kowane fanni na mulki.”
Lakca mai taken ‘Zaben 2023: Musulmai da kuma tasirin rinjaye na adalci’, ya kasance wanda Afeez Oladosu ya gabatar yayin taron.
Oladosu ya bukaci Musulmin Oyo da su yi rajista tare da karbar katin zabe na dindindin (PVC) gabanin babban zabe na 2023.
Ya kuma bukaci masu zabe da su zabi shugabanni masu tsoron Allah cikin hikima a lokacin zaben.