fidelitybank

Gwamnati na ta gyara hanoyiyi da dama a Najeriya

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce, gwamnatinsa ta fara aikin gine-gine tare da gyara ayyukan tituna da sauran ababen more rayuwa da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar ‘yan Najeriya.

Shugaban wanda ya samu wakilcin ministan albarkatun ruwa Alhaji Suleiman Adamu ya bayyana haka a Birniwa yayin kaddamar da aikin titin Hadejia zuwa Nguru mai tsawon kilomita 33 wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 7.9.

Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta gina tare da gyara hanyoyi da dama da kuma gadoji a fadin kasar nan daga shekarar 2015 zuwa yau.

Ya kuma gargadi hukumomin gwamnati da abin ya shafa da su aiwatar da dokar takaita gudun kilomita 100 akan hanyoyin Najeriya domin rage hadurran da ba dole ba.

Har ila yau, ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Raji Fasola, ya ce gwamnatin shugaba Buhari ta samar da ababen more rayuwa a dukkan shiyyoyin siyasar kasar nan guda shida.

Fasola ya ce an kammala ayyuka da dama kuma an kaddamar da su, yayin da wasu kuma ana kan kammala kuma nan ba da dadewa ba za a kaddamar da su.

Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yabawa gwamnatin tarayya, karkashin shugaba Buhari kan ayyukan tituna.

Gwamnan wanda mataimakinsa Malam Umar Namadi ya wakilta, ya ce jihar ta ci gajiya sosai daga ayyukan gwamnatin tarayya daga shekarar 2015 zuwa yau.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp