fidelitybank

Gwamnati na ta gyara hanoyiyi da dama a Najeriya

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce, gwamnatinsa ta fara aikin gine-gine tare da gyara ayyukan tituna da sauran ababen more rayuwa da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar ‘yan Najeriya.

Shugaban wanda ya samu wakilcin ministan albarkatun ruwa Alhaji Suleiman Adamu ya bayyana haka a Birniwa yayin kaddamar da aikin titin Hadejia zuwa Nguru mai tsawon kilomita 33 wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 7.9.

Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta gina tare da gyara hanyoyi da dama da kuma gadoji a fadin kasar nan daga shekarar 2015 zuwa yau.

Ya kuma gargadi hukumomin gwamnati da abin ya shafa da su aiwatar da dokar takaita gudun kilomita 100 akan hanyoyin Najeriya domin rage hadurran da ba dole ba.

Har ila yau, ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Raji Fasola, ya ce gwamnatin shugaba Buhari ta samar da ababen more rayuwa a dukkan shiyyoyin siyasar kasar nan guda shida.

Fasola ya ce an kammala ayyuka da dama kuma an kaddamar da su, yayin da wasu kuma ana kan kammala kuma nan ba da dadewa ba za a kaddamar da su.

Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yabawa gwamnatin tarayya, karkashin shugaba Buhari kan ayyukan tituna.

Gwamnan wanda mataimakinsa Malam Umar Namadi ya wakilta, ya ce jihar ta ci gajiya sosai daga ayyukan gwamnatin tarayya daga shekarar 2015 zuwa yau.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp