fidelitybank

Gwamnati na neman mafita a kan dasa bam da ƴan Ta’adda ke yi

Date:

Mai ba shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya yi kira da a ƙara kaimi da kuma samar da hanyoyi na kawo karshen ababen fashewa da ƙungiyoyin ƴan ta’dda a yammacin Afrika ke amfani da wasu wajen kai hare-hare.

Ribadu ya bayyana haka ne a wani taron masu ruwa da tsaki na ganin an haɗa kai wajen daƙile amfani da ababen fashewa a yammacin Afirka da aka buɗe a Abuja, ranar Talata.

Mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkar tsaro ya ce barazanar ayyukan ƴan ta’dda ba su da iyaka, inda ya ƙara da cewa sai masu ruwa da tsaki sun haɗa kai, kafin za a samu damar magance matsalar.

Ya ƙarfafa gwiwar mahalarta taron cewa su shiga a dama da su ta hanyar tattaunawa, samar da hanyoyi da kuma aiki tare don laluɓo mafita da za ta taimaka wajen daƙile ayyukan ta’ddanci da ke yi wa al’ummomi a yammacin Afirka barazana.

“Muna shirin samar da dabaru na zamani waɗanda za su taimaka mana wajen daƙile amfani da ababen fashewa.

“Shawarwari da za a samu a wannan taro suna da muhimmanci wajen tsara yadda za mu kare al’ummomin mu daga barazanar ababen fashewa,” in ji Ribadu.

Shi ma lokacin da yake magana a wajen taron – jakadan Aljeriya a Najeriya, Hocine Mezoued, ya ce dole ne ƙasashen Afirka su ɗauki matakan yaƙi da ta’addanci idan har ana so kawo karshen matsalar.

Ya ce matakan za su kuma taimaka wajen daƙile sabbin hanyoyin zamani da ƴan ta’ddan ke amfani da su wajen kai hare-hare.

A cewarsa, ababen fashewa ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyi da ƴan ta’dda suka fi amfani da su wajen far wa al’ummomi a faɗin yammacin Afirka da kuma ƙasashen da ke yankin Sahel.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp