fidelitybank

Gwamnati na neman mafita a kan dasa bam da ƴan Ta’adda ke yi

Date:

Mai ba shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya yi kira da a ƙara kaimi da kuma samar da hanyoyi na kawo karshen ababen fashewa da ƙungiyoyin ƴan ta’dda a yammacin Afrika ke amfani da wasu wajen kai hare-hare.

Ribadu ya bayyana haka ne a wani taron masu ruwa da tsaki na ganin an haɗa kai wajen daƙile amfani da ababen fashewa a yammacin Afirka da aka buɗe a Abuja, ranar Talata.

Mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkar tsaro ya ce barazanar ayyukan ƴan ta’dda ba su da iyaka, inda ya ƙara da cewa sai masu ruwa da tsaki sun haɗa kai, kafin za a samu damar magance matsalar.

Ya ƙarfafa gwiwar mahalarta taron cewa su shiga a dama da su ta hanyar tattaunawa, samar da hanyoyi da kuma aiki tare don laluɓo mafita da za ta taimaka wajen daƙile ayyukan ta’ddanci da ke yi wa al’ummomi a yammacin Afirka barazana.

“Muna shirin samar da dabaru na zamani waɗanda za su taimaka mana wajen daƙile amfani da ababen fashewa.

“Shawarwari da za a samu a wannan taro suna da muhimmanci wajen tsara yadda za mu kare al’ummomin mu daga barazanar ababen fashewa,” in ji Ribadu.

Shi ma lokacin da yake magana a wajen taron – jakadan Aljeriya a Najeriya, Hocine Mezoued, ya ce dole ne ƙasashen Afirka su ɗauki matakan yaƙi da ta’addanci idan har ana so kawo karshen matsalar.

Ya ce matakan za su kuma taimaka wajen daƙile sabbin hanyoyin zamani da ƴan ta’ddan ke amfani da su wajen kai hare-hare.

A cewarsa, ababen fashewa ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyi da ƴan ta’dda suka fi amfani da su wajen far wa al’ummomi a faɗin yammacin Afirka da kuma ƙasashen da ke yankin Sahel.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp