fidelitybank

Gwamnati na neman mafita a kan dasa bam da ƴan Ta’adda ke yi

Date:

Mai ba shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya yi kira da a ƙara kaimi da kuma samar da hanyoyi na kawo karshen ababen fashewa da ƙungiyoyin ƴan ta’dda a yammacin Afrika ke amfani da wasu wajen kai hare-hare.

Ribadu ya bayyana haka ne a wani taron masu ruwa da tsaki na ganin an haɗa kai wajen daƙile amfani da ababen fashewa a yammacin Afirka da aka buɗe a Abuja, ranar Talata.

Mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkar tsaro ya ce barazanar ayyukan ƴan ta’dda ba su da iyaka, inda ya ƙara da cewa sai masu ruwa da tsaki sun haɗa kai, kafin za a samu damar magance matsalar.

Ya ƙarfafa gwiwar mahalarta taron cewa su shiga a dama da su ta hanyar tattaunawa, samar da hanyoyi da kuma aiki tare don laluɓo mafita da za ta taimaka wajen daƙile ayyukan ta’ddanci da ke yi wa al’ummomi a yammacin Afirka barazana.

“Muna shirin samar da dabaru na zamani waɗanda za su taimaka mana wajen daƙile amfani da ababen fashewa.

“Shawarwari da za a samu a wannan taro suna da muhimmanci wajen tsara yadda za mu kare al’ummomin mu daga barazanar ababen fashewa,” in ji Ribadu.

Shi ma lokacin da yake magana a wajen taron – jakadan Aljeriya a Najeriya, Hocine Mezoued, ya ce dole ne ƙasashen Afirka su ɗauki matakan yaƙi da ta’addanci idan har ana so kawo karshen matsalar.

Ya ce matakan za su kuma taimaka wajen daƙile sabbin hanyoyin zamani da ƴan ta’ddan ke amfani da su wajen kai hare-hare.

A cewarsa, ababen fashewa ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyi da ƴan ta’dda suka fi amfani da su wajen far wa al’ummomi a faɗin yammacin Afirka da kuma ƙasashen da ke yankin Sahel.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp