Yayin da al’umma jihohin areywacin ƙasar nan ke ci gaba da kokawa dangane da rashin wutar lantarki na tsawon kwanaki, majalisar dattawa ta ce, gwamanti na ɗaukar matakai na tsaro wajen ganin an shawo kan matsalar.
Majalisar dattawan ta ce hari da wasu ƴan bindiga masu iƙirarin jihadi suka kai kan turakun wutar lantarki ne ya janyo matsalar da ake fama da ita a arewacin ƙasar.
Tun da fari dai kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya TCN ya ce, tangarɗa aka samu a layin lantarki na Ugwaji-Apir mai ƙarfin 330kV, wanda ya yi sanadiyar rashin wuta a Arewacin ƙasar nan.
Sanata Barau Jibrin shi ne mataimakin shugaban majalisar datijjai, ya koka kan yawan lalacewar da babban layin lantarki na Najeriya ya yi har sau uku a baya bayan nan, wanda hakan ya sa suka fara tattaunawa da ɓangaren gwamanti domin ɗaukar matakai na koma amfani da wutar lanatarki mai amfani da hasken rana don magance wannan matsala.