fidelitybank

Gwamnati ki gaggauta mayar da farashin man fetur yadda yake a baya – SERAP

Date:

Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a Najeriya, ta buƙaci a gaggauta janye ƙarin farashin man fetir a ƙasar.

Ƙungiyar ta buƙaci shugaba Bola Tinubu ”ya umarci kamfanin mai na Najeriya, NNPCL ya gaggauta soke ƙarin farashin man da yayi, wanda shi ne karo na biyu a cikin wata ɗaya, har zuwa lokacin da za a samu hukuncin kotu a kan ƙarar da aka shigar domin ƙalubalantar ƙarfin ikon kamfanin NNPCL game da ƙara farashin mai a ƙasar.”

A watan da ya gabata, ƙungiyar SERAP ta shigar da ƙara, inda take neman kotu ta tilastawa shugaba Tinubu da kamfanin NNPCL ”mayar da farashin man fetir a yadda ya ke kafin ƙarin, da kuma neman a gudanar da bincike a kan almundahanar da ake zargin ana tafkawa a kamfanin NNPCL.”

Mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya ce “Sabon ƙarin farashin man fetir ɗin a daidai lokacin da ake gaban kotu domin tantance ƙarfin ikon masu alhakin ƙara farashin, cin fuska ne ga tafarkin shari’a”

SERAP ta buƙaci shugaba Tinubu ya gaggauta bayar da umarnin dakatar da sabon farashin man har zuwa lokacin da kotu ta yanke hukunci a game da ruɗanin da aka shiga na neman tantanci wanda ke da ƙarfin ikon ƙara farashin mai a Najeriya.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp