Gwamna Udom Emmanuel na jihar Akwa Ibom kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, ya roki gwamnatin tarayya da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da su kawo karshen yajin aikin da suke yi a sake bude jami’o’i, domin ɗalibai su koma makaranta.
A wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar Udom Emmanuel, Mista Bola Bolawole ya fitar a madadinsa, Emmanuel ya ce, lokaci ya yi da ya kamata bangarorin biyu na gwamnatin tarayya da ASUU su sauka daga kan dokinsu da kuma kaucewa bala’i da ka iya tunkaro kasar nan. Tsarin ilimi gaba daya idan ba a gaggauta janye yajin aikin ASUU ba, aka sake bude jami’o’inmu domin yin karatu.
“Tuni dai an fara tattaunawa a wasu kasashen ketare, inda al’ummarmu, musamman matasanmu ke neman aikin yi musamman ma noma da kiwo, domin karbo takardar shaidar jami’a daga Najeriya. Allah ya kiyaye faruwar hakan! Abubuwan da ke faruwa a kan mutanenmu sun fi tunanin fiye da yadda ake ji.