fidelitybank

Gwamnan Zamfara ya bayar da miliyan 100 ga mutanen da ambaliya ya shafa

Date:

Gwamnan jihar Zamafar Dauda Lawal Dare ya bai wa al’ummar yankin Gummi da suka fuskanci bala’in ambaliya tallafin naira miliyan 100.

Cikin wata sanarwa da sakatare yaɗa labaran gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce gwamnan ziyarci garin Gummi ranar Asabar, domin jajanta wa mutanen da bala’in ambaliyar ta shafa.

Garin Gummi ya fuskanci mummunar ambaliya a ‘yan kwanakin baya-bayan nan , lamarin da ya haddasa asarar dukiya mai dimbin yawa.

Dauda Lawal ya ce ya je garin ne domin jajanta wa mutanen garin kan abin da ya faru.

Gwamnan ya kuma kai musu kayayyakin tallafi domin rage musu raɗaɗin asarar da suka yi a lokacin ambaliyar.

“Ina so na yi amfani da wannan damar don sanar da ku cewa na ba ku tallafin buhu 10,000 na abinci da ya haɗa da shinkafa da masara da gero domin raba wa mutane da bala’in ya shafa. Haka kuma a madadin gwamnatin jihar Zamfara na bayar da tallafin naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ta shafa”, in ji shi.

Gwamnan ya kuma ƙara da cewa gwamnati za ta bai wa mutanen da ambaliyar ta shafa filaye a wuraren da ba su da hatsarin ambaliya domin sake gina gidajensu.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp