Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya bai wa ɗaliban jihar su 16 da suka karanci aikin jinya, a jami’ar Sudan aiki.
A ranar Alhamis ne gwamnan ya gabatar wa ɗaliban takardunsu na shaidar kammala karatu da jami’ar ta aiko musu a fadarsa gwamnati da ke birnin Gusau.
Cikin wata sanarwar da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ya ce a 2023 ne gwamnatin jihar ta kwaso ɗaliban Zamfara 66 da ta tura Sudan domin karatu bayan ɓarkewar rikicin ƙasar.
”16 daga cikin ɗaliban masu karantar aikin jinya ne da ke shekarar ƙarshe a karatunsu, waɗanda jarrabawar ƙarshe ce kawai ta rage su kammala karatun, inda gwamnatin jihar ta ɗauki matakin taimaka wa ɗaliban”, in ji sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta haɗa kai da hukumar gudunarwar jami’ar, domin bai wa ɗaliban 16 damar rubuta jarrabawar tasu ta ƙarshe, wadda aka yi a Najeriya.
Daga nan kuma jami’ar ta aika wa ɗaliban takardun shaidar kammala karatun nasu, wadda kuma gwamnan ya gabatar musu a lokacin da ya yi musu albishirn ba su aikin a gwamnatin jihar.