fidelitybank

Gwamnan Zamfara ya baiwa Ɗalibai aiki su 16 da yaƙin Sudan ya koro su

Date:

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya bai wa ɗaliban jihar su 16 da suka karanci aikin jinya, a jami’ar Sudan aiki.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya gabatar wa ɗaliban takardunsu na shaidar kammala karatu da jami’ar ta aiko musu a fadarsa gwamnati da ke birnin Gusau.

Cikin wata sanarwar da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ya ce a 2023 ne gwamnatin jihar ta kwaso ɗaliban Zamfara 66 da ta tura Sudan domin karatu bayan ɓarkewar rikicin ƙasar.

”16 daga cikin ɗaliban masu karantar aikin jinya ne da ke shekarar ƙarshe a karatunsu, waɗanda jarrabawar ƙarshe ce kawai ta rage su kammala karatun, inda gwamnatin jihar ta ɗauki matakin taimaka wa ɗaliban”, in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta haɗa kai da hukumar gudunarwar jami’ar, domin bai wa ɗaliban 16 damar rubuta jarrabawar tasu ta ƙarshe, wadda aka yi a Najeriya.

Daga nan kuma jami’ar ta aika wa ɗaliban takardun shaidar kammala karatun nasu, wadda kuma gwamnan ya gabatar musu a lokacin da ya yi musu albishirn ba su aikin a gwamnatin jihar.

Go back

Your message has been sent

Warning
Warning
Warning
Warning

Warning.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp