fidelitybank

Gwamnan Zamfara ya baiwa Ɗalibai aiki su 16 da yaƙin Sudan ya koro su

Date:

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya bai wa ɗaliban jihar su 16 da suka karanci aikin jinya, a jami’ar Sudan aiki.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya gabatar wa ɗaliban takardunsu na shaidar kammala karatu da jami’ar ta aiko musu a fadarsa gwamnati da ke birnin Gusau.

Cikin wata sanarwar da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ya ce a 2023 ne gwamnatin jihar ta kwaso ɗaliban Zamfara 66 da ta tura Sudan domin karatu bayan ɓarkewar rikicin ƙasar.

”16 daga cikin ɗaliban masu karantar aikin jinya ne da ke shekarar ƙarshe a karatunsu, waɗanda jarrabawar ƙarshe ce kawai ta rage su kammala karatun, inda gwamnatin jihar ta ɗauki matakin taimaka wa ɗaliban”, in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta haɗa kai da hukumar gudunarwar jami’ar, domin bai wa ɗaliban 16 damar rubuta jarrabawar tasu ta ƙarshe, wadda aka yi a Najeriya.

Daga nan kuma jami’ar ta aika wa ɗaliban takardun shaidar kammala karatun nasu, wadda kuma gwamnan ya gabatar musu a lokacin da ya yi musu albishirn ba su aikin a gwamnatin jihar.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp