fidelitybank

Gwamnan Yobe ya janye dokar hawa Babur a jihar bayan shekaru 10

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya dage dokar hana amfani da babura a yankunan Arewaci da Kudancin jihar.

Hakan dai ya biyo bayan komawar al’amura a galibin yankunan tare da komawar hukumomin farar hula.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Nguru, domin jajanta wa jama’a kan aukuwar gobara da ta lalata kadarori na miliyoyin Naira a kasuwar Nguru.

Buni ya ce”A yanzu mazauna garin sun samu damar hawan Babura, domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

“Da wannan ne mu ke gudanar da wani bangare na yakin neman zabe, domin dawo da zaman lafiya a jihar da kuma ba da damar amfani da Babura, domin bukatun jama’a,” inji shi.

Kananan hukumomi 10 da aka amince su yi amfani da baburan sun hada da Fika, Nangere, Fune, Potiskum, Jakusko, Bade, Nguru, Karasuwa, Yusufari da Machina.

Sai dai matakin ya ta’allaka ne da wasu sharudda takwas da masu tuka mota suka cika, daya daga cikinsu shi ne cewa dole ne su rika gudanar da aiki daga karfe shida na safe zuwa karfe 6 na yamma a kowace rana kuma kada a yi amfani da su wajen tallan kabu-kabu (Achaba). Mahayi daya ne kawai za a yarda ba tare da wani mutum a kan babur ba.

Ya ce”Dole ne a samar da ingantaccen rajista, lasisi da takaddun duk babura da masu keke a cikin kananan hukumomin da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Yobe (YROTA) ke aiwatarwa”. A cewar Buni.

Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar Yobe ta haramta amfani da babura a daidai lokacin da rikicin Boko Haram ya barke a cikin shekaru 12 da suka gabata.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp