fidelitybank

Gwamnan Yobe ya janye dokar hawa Babur a jihar bayan shekaru 10

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya dage dokar hana amfani da babura a yankunan Arewaci da Kudancin jihar.

Hakan dai ya biyo bayan komawar al’amura a galibin yankunan tare da komawar hukumomin farar hula.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Nguru, domin jajanta wa jama’a kan aukuwar gobara da ta lalata kadarori na miliyoyin Naira a kasuwar Nguru.

Buni ya ce”A yanzu mazauna garin sun samu damar hawan Babura, domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

“Da wannan ne mu ke gudanar da wani bangare na yakin neman zabe, domin dawo da zaman lafiya a jihar da kuma ba da damar amfani da Babura, domin bukatun jama’a,” inji shi.

Kananan hukumomi 10 da aka amince su yi amfani da baburan sun hada da Fika, Nangere, Fune, Potiskum, Jakusko, Bade, Nguru, Karasuwa, Yusufari da Machina.

Sai dai matakin ya ta’allaka ne da wasu sharudda takwas da masu tuka mota suka cika, daya daga cikinsu shi ne cewa dole ne su rika gudanar da aiki daga karfe shida na safe zuwa karfe 6 na yamma a kowace rana kuma kada a yi amfani da su wajen tallan kabu-kabu (Achaba). Mahayi daya ne kawai za a yarda ba tare da wani mutum a kan babur ba.

Ya ce”Dole ne a samar da ingantaccen rajista, lasisi da takaddun duk babura da masu keke a cikin kananan hukumomin da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Yobe (YROTA) ke aiwatarwa”. A cewar Buni.

Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar Yobe ta haramta amfani da babura a daidai lokacin da rikicin Boko Haram ya barke a cikin shekaru 12 da suka gabata.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp