fidelitybank

Gwamnan Sokoto ya raba kayan abinci da miƙa miliyan 20 ga mutanen da suka shiga taskun ƴan bindiga

Date:

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya bai wa al’ummar yankin Sabon Birni da ayyukan ƴan bindiga ya shafa tallafin sama da naira miliyan 20 tare da rarraba magunguna da kayan abinci.

Ya kuma yi alƙawarin ɗaukar nauyin kuɗin maganin mutanen da suka ji rauni sakamakon hare-haren ƴan bindiga a ƙaramar hukumar da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne bayan ziyarar da ya kai tare da Sanata Aliyu Wamakko zuwa ƙaramar hukumar domin jajanta wa mutanen da hare-haren ƴan bindiga suka shafa.

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Gwamnan ya ce zai ci gaba da tallafa wa al’ummar yankin tare da kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Ya kuma bayyana damuwa kan faruwar hare-haren inda ya ce yana matuƙar kaɗuwa duk lokacin da aka samu afkuwar harin ƴan bindiga a wani yanki na jihar.

A cewarsa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba domin daƙile matsalar rashin tsaro a jihar ta Sokoto.

Ahmad Aliyu ya kuma ce za su ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro inda ya sanar da basu motoci 100 da kuma horas da ƴan vigilante 2,000 domin su ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Ya ƙara da cewa za a bai wa ƴan vigilanten babura 700 domin sauƙaƙa ayyukansu ƙarƙashin kulawar hukumomin tsaro.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp