Gwamnan jihar Rivers a kudancin Najeriya, Siminalayi Fubara, ya biya wa maniyyata aikin Hajjin bana daga jihar cikon naira miliyan daya da dubu dari tara na kuɗin kujerun.
A farkon makon nan ne Hukumar Alhazan Najeriya ta bayyana ƙarin kudin, tana mai alaƙanta matakin da faɗuwar darajar naira.
Gwamnan dai ya dauki wannan mataki ne a kokarin cika alkawarin da ya yi wa jama’ar jihar a lokacin yaƙin neman zabe, cewa zai tafi da kowa a gwamnatin ba tare da nuna bambancin addini ko ƙabila ba.
Alhaji Yakubu Aliyu, daya ne daga cikin shugabannin ‘yan arewacin Najeriya mazauna jihar ta Rivers, kuma ya yi karin bayani a hirarsa da Abdussalam Ibrahim Ahmed.