Rahotanni na cewa wani mummunan turmutsutsu da aka samu a wata makarantar Islamiyya a birnin Badun (Ibadan) na jihar Oyo, ya janyo mutuwar kananan yara da dama jiya Laraba.
Lamarin ya faru ne a unguwar Bashorun, yayin wani biki da yaran ke gudanarwa, sai dai har kawo yanzu, ba a hakikance adadin wadanda lamarin ya rutsa da su ba.
Wata sanarwar kwamishinan watsa labaran jihar Dotun Oyelade, ta ce an kwashi wasu daga cikin wadanda suka samu raunuka zuwa asibitoci daban daban da ke kwaryar birnin domin kula da lafiyarsu.
Zuwa yanzu ba a bayyana musabbabin faruwar lamarin ba, sai dai mazauna yankin sun ce sama da yara dubu biyar ne suka taru a wurin da ake gudanar da bikin, inda masu shirya gasar suka yi alkawarin bayar da muhimman kyautuka, ciki har da tallafin karatu.
Turmutsutsun ya soma ne lokacin da manyan masu shirya taron suka isa wurin da za a fara taron.
“Ana kira ga iyayen da ke neman inda ‘ya’yansu suke da su duba asibitocin da suke kwance domin tantance ko suna wuraren” inji kwamishinan watsa labaran jihar.
Gwamnan jihar ta Oyo, Seyi Makinde, ya wallafa wani sako a shafinsa na Twitter wato X, inda ya ce an dauki kwararan matakai don ganin hakan ba ta sake faruwa ba, kana za a gudanar da bincike don gano ainihin abun da ya faru.
Ya kara da cewa za a hukunta duk wanda aka gano yana da hannu a faruwar bala’in.