fidelitybank

Gwamnan Oyo ya bayar da umarni a binciki wata Islamiyya da ta yi taro Yara da dama suka mutu

Date:

 

Rahotanni na cewa wani mummunan turmutsutsu da aka samu a wata makarantar Islamiyya a birnin Badun (Ibadan) na jihar Oyo, ya janyo mutuwar kananan yara da dama jiya Laraba.

Lamarin ya faru ne a unguwar Bashorun, yayin wani biki da yaran ke gudanarwa, sai dai har kawo yanzu, ba a hakikance adadin wadanda lamarin ya rutsa da su ba.

Wata sanarwar kwamishinan watsa labaran jihar Dotun Oyelade, ta ce an kwashi wasu daga cikin wadanda suka samu raunuka zuwa asibitoci daban daban da ke kwaryar birnin domin kula da lafiyarsu.

Zuwa yanzu ba a bayyana musabbabin faruwar lamarin ba, sai dai mazauna yankin sun ce sama da yara dubu biyar ne suka taru a wurin da ake gudanar da bikin, inda masu shirya gasar suka yi alkawarin bayar da muhimman kyautuka, ciki har da tallafin karatu.

Turmutsutsun ya soma ne lokacin da manyan masu shirya taron suka isa wurin da za a fara taron.

“Ana kira ga iyayen da ke neman inda ‘ya’yansu suke da su duba asibitocin da suke kwance domin tantance ko suna wuraren” inji kwamishinan watsa labaran jihar.

Gwamnan jihar ta Oyo, Seyi Makinde, ya wallafa wani sako a shafinsa na Twitter wato X, inda ya ce an dauki kwararan matakai don ganin hakan ba ta sake faruwa ba, kana za a gudanar da bincike don gano ainihin abun da ya faru.

Ya kara da cewa za a hukunta duk wanda aka gano yana da hannu a faruwar bala’in.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp