Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya gayyaci jagororin zanga-zangar tsadar rayuwa da ake shirin gudanarwa da sauran masu ruwa da tsaki daga jami’an tsaro da Æ™ungiyoyin fararen hula domin tattaunawa game da batun a gobe Litinin.
Cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Mallam Olawale Rasheed, ya fitar, ya ce gwamnan ya umarci wata tawagar wakilansa ta tuntuɓi wakilan ƙungiyoyin fararen hula da na ɗalibai domin zaman tattaunawa kan halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki.
Gwamna ya kuma buÆ™aci shugabannin hukumomin ‘yansanda da sauran jami’an tsaro su halarci zaman, inda za a bai jagororin zanga-zangar damar bayyana irin damuwar da ke zukatansu.
“Zaman zai bayar da dama ga duka É“angarorin su bayyana matsalolinsu da abin da suke so gwamnatoci a matakai daban-daban su yi domin magance matsalolin”
“Za kuma mu É—auki abin da muka tattauna a zaman domin kai wa jagororin gwamnati, kama daga ni kaina a a matsayina na gwamna zuwa shugaban Æ™asa a Abuja domin aiki da shi”, kamar yadda sanarwar ta ambato gwamnan na bayani.
Mista Adeleke ya kuma ce zaman zai bai wa gwamnati damar bayyana wa al’umma abin da take yi don magance matsalar tattalin arziki da Æ™asar ke fuskanta.