Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya gabatar da kasafin kudi N273, 908, 997, 410:00 ga majalisar dokokin jihar Osun.
Kasafin kudin ya zama wani bangare na lissafin Kasafin Kudi na 2024.
Gwamna Adeleke yayin da yake gabatar da kasafin kudin mai taken: Kasafin Kudi na Gyara da Farfadowa a zauren majalisar, a ranar Alhamis, ya ce an raba kasafin zuwa N165, 654, 976, 700:00 na kashe-kashe na yau da kullun da kuma N108, 254, 020, 710:00 na kashe kudade. .
A nasa jawabin, Adeleke ya ce, “ kasafin kudin na da nufin sake gina tattalin arzikin jihar da ya durkushe.
“Wannan gabatar da kasafin kudin ya yi dai-dai da dokokin da ake da su a jihar wadanda suka tanadi gabatar da kasafin ga majalisar kafin karshen shekara.
Yayin da yake godewa majalisar bisa fahimtarsu, Gwamnan ya ba da tabbacin cewa jihar za ta kai ga ci gaba.
Ya kuma nemi goyon bayan majalisar a shekaru masu zuwa.
Tun da farko, Kakakin Majalisar, Adewale Egbedun ya bayyana shirin majalisar na yin aiki da bangaren zartaswa na gwamnati don ganin an samu nasarar aiwatar da kasafin kudin.
“Wannan kasafin kudin za a amince da shi tare da azama mai karfi.
“Majalisar za ta gabatar da kasafin kudin da zai magance kalubalen da jihar ke fuskanta.”