Gwamnan jihar Neja kuma shugaban kungiyar gwamnonin jihohin arewa ta tsakiya (NCSGF), Abubakar Sani Bello, ya jajantawa gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule bisa rashin babban dansa, Hassan Abdullahi Sule.
Bello a cikin sakon ta’aziyyar ya bayyana marigayin a matsayin matashi mai hazaka kuma haziki wanda ke da kyakkyawar makoma.
Gwamnan jihar Neja ya ce: “Hakika abin bakin ciki ne da bacin rai a rasa da, babban da a kan hakan kuma tun yana karami. Haqiqa qwaya ce mai daci a hadiye amma Allah da ya ba shi damar ta’aziya ga ‘yan uwa da sauran al’ummar Jihar Nasarawa baki xaya.”
Shugaban NCSGF ya umurci abokin aikin sa da su dogara ga Allah a wannan lokaci mai wahala domin samun ta’aziyyar da ake bukata.
Daga nan ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayin ya jikansa da rahama, ya kuma saka masa da Aljannar Firdausi tare da baiwa ‘yan uwa hakurin jure rashin da ba za a iya kwatantawa ba.