fidelitybank

Gwamnan Neja ya kafa dokar ta bace a yankin Lambata

Date:

Gwamnan jihar Neja, Abubakar Bello, ya kafa dokar hana fita a garin Lambata dake karamar hukumar Gurara ta jihar, biyo bayan wani kazamin fada da yayi sanadiyar mutuwar hakimin Lambata Mohammed Abdulsafur.

Sakataren gwamnatin jihar (SSG), Ahmed Ibrahim Matane ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in yada labarai na ofishin SSG, Lawal Tanko ya fitar.

Matane ya kara da cewa gwamnan ya bada umarnin a sanya dokar hana fita a garin na Lambata daga karfe 6:00 na yamma zuwa karfe 6:00 na safe daga ranar Lahadi 15 ga watan Janairu, 2023 har zuwa wani lokaci.

SSG ta bayyana cewa an sanya dokar ne domin a taimakawa jami’an tsaro wajen daidaita al’amura a yankin, da ceton rayuka, da kuma ba da damar maido da doka da oda.

A cewarsa, ā€œGwamnati ta yi Allah wadai da ta’addanci da rashin bin doka da oda da aka samu a garin Lambata.ā€

Sanarwar ta kara da cewa, gwamnatin jihar ta yi kira ga mazauna yankin da su baiwa jami’an tsaro hadin kai a aikin gaggawa na maido da zaman lafiya a garin Lambata, yayin da ta bukaci hukumomin tsaro da su tabbatar da aiwatar da dokar hana fita.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp