Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, ya yi yunkurin hana gwamnoni da ministoci saka sunansa, amma gwamnan Kogi Yahaya Bello ya bijire masa.
Buhari ya bayyana hakan ne a wani shirin kai tsaye da tashar talabijin ta Arise TV ta watsa na ziyarar sa a jihar Kogi.
Buhari ya kaddamar da sabuwar Jamiāar Kimiyya da Fasaha ta Confluence a Osara, Asibitin Reference da ke Okene, da hanyoyin sadarwa na garin Idah, Okene da kuma fadin kananan hukumomin uku na majalisar dattawa.
Sauran ayyukan sun hada da Ganaja Flyover, Model Science Secondary School, Muhammadu Buhari Square da Civic Centre a Lokoja.
āIna godiya ga Gwamna da alāummar jihar Kogi da suka sanya min suna (Muhammadu Buhari Square and Civic Centre). A nan, dole ne in nutse; Na yi yunkurin hana gwamnoni da ministoci sunana ayyuka, amma Gwamna ya bijire mani a nan,ā inji shi.