fidelitybank

Gwamnan Katsina ya sanya hannu da kamfanin Faransa na samawa jihar wutar lantarki

Date:

Gwamnatin jihar Katsina ta rattaba hannu da wani kamfanin kasar Faransa mai suna Ocean Solutions Energie domin bunkasa wutar lantarki a jihar.

Yarjejeniyar ta yi daidai da dokar samar da wutar lantarki ta 2023 wacce ta karkasa hanyoyin samar da makamashi da hade hanyoyin da ake sabunta su a cikin wutar lantarkin Najeriya.

Har ila yau, yana cikin cika burin ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya (SDGs) 7 akan makamashi mai araha da tsafta.

Gwamnan jihar, Malam Dikko Radda da mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin wutar lantarki da makamashi, Dakta Hafiz Ahmed, sun sanya hannu kan yarjejeniyar, bayan wata tattaunawa da takwarorinsu na ci gaba da masana’antu a birnin Paris na kasar Faransa.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan, Ibrahim Mohammed, a wata sanarwa da ya fitar jiya Lahadi, ya ce kamfanin na kasar Faransa wanda ya kware wajen bunkasa ayyukan makamashi a nahiyar Afirka, ya samu wakilcin shugaban kamfanin, Mista Minkaila Salami.

Sanarwar ta ce: “A bisa wadannan manufofi, Gwamna Radda ya bayyana shirin kafa wata karamar tashar samar da wutar lantarki a wani bangare na aikin gwaji.

“Gwamnan ya lura cewa shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da ingantaccen makamashi mai sabuntawa ga al’ummomin yankin kuma zai zama abin koyi ga ci gaban wutar lantarki a nan gaba a fadin madatsun ruwa 43 na jihar.

“Gwamnatin jihar Katsina ta kuduri aniyar bayar da tallafin kudi domin ganin an samu nasarar girka tashar wutar lantarki da kuma dorewar dogon lokaci.”

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp