fidelitybank

Gwamnan Katsina ya raba buhun shinkafa 40,000 na rage radadi

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Raɗɗa ya ce ya ba da umarnin raba shinkafa buhu 40,000 nan take, ga al’ummar jihar da nufin rage raɗaɗin matsin rayuwa bayan cire tallafin man fetur a Najeriya.

Wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Gwamna Raɗɗa ya ce gwamnatinsa ta sayo shinkafar ne daga kuɗin rage raɗaɗi da jihar ta karɓa daga gwamnatin tarayya.

Ya kuma ce ya amince da kafa kwamitoci don raba shinkafar a matakan ƙananan hukumomi da mazaɓu na jihar.

Sai dai, saɓanin naira biliyan biyar da Majalisar kula Tattalin Arziƙin Ƙasa ta ambata tun farko bayan wani taro da ta gudanar kwanan baya, Gwamna Umar Raɗɗa ya ce gwamnatinsa ta sayo shinkafar ne da naira biliyan biyu da gwamnatin tarayya ta saki.

Haka zalika ya bayyana kafa kwamitocin bibiya da sa ido don ganin yadda aikin rabon shinkafar zai kasance.

Umar Dikko Raɗɗa ya kuma yi gargaɗin cewa duk mutumin da aka samu da ƙoƙarin cin amana a aikin rabon shinkafar, kai tsaye ko a kaikaice, to zai fuskanci fushin hukuma.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp