Gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda, ya shiga tawagar jami’an tsaro don daƙile wani harin da ‘yan bindiga suka suka ƙauyen Zakka da ke ƙaramar hukumar Safana a jihar.
Cikin wata sanarwa da satakaren yaɗa labaran gwamnan, Kaula Mohammed, ya fitar, ya ce tawagar jami’an tsaron ta samu nasara kuɓutar da wani mutum mai shekara 33 da ‘yan bingidar suka kama a lokacin da suka kai harin.
Sanarwar ta ce, da farko gwamnan ya je Safana ne domin ƙaddamar da wani shirin tallafi da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar, Abduljalal Runka, ya shirya a lokacin da ak yi wa jami’an tsaro kiran gaggawa kan harin da ‘yan bindigar suka kai ƙauyen na Zakka.
Bayan samun rahoton ne kuma, sai gwamna ya gaggauta katse taron da yake halarta, inda nan take ya nufi ƙauyen tare da sauran jami’an tsaro.
“Gwamna Radda tare da wasu mambobin tawagarsa sun i sahun jami’an tsaro da suka haɗar da ‘yan sanda da sojojin saman rundunar Hadarin Daji, da na ƙasa, da kuma jami’an tsaron sa-kai da ya ƙaddamar”, in ji sanarwar
An yi arangama da ‘yan bindigar kafin su tsre zuwa cikin tsaunuka.
“Bayan fafatawa mai zafi na tsawon miti 30 da ‘yan bindigar, jami’an tsaron sun samu nasarar kuɓutar da wani mutum mai shekara 33”
Sanarwar ta kara da cewa ‘yan bindigar sun tsere ba tare da kashe wasu daga cikinsu ba.
Bayan daƙile hari ne kuma, Gwamna Radda ya bayar da umarnin gaggauta kai mutumin da aka ƙubutar asibiti bayan da ‘yan bindigar suka harbe shi a ƙafa, in ji sanarwar.
Dama dai gwamnan ya sha yin alwashin shiga daji domin yaƙar ‘yan bindiga a lokutan yaƙin neman zaɓensa.