fidelitybank

Gwamnan Katsina shiga tawagar jami’an tsaro na yakar ‘yan bindiga

Date:

Gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda, ya shiga tawagar jami’an tsaro don daƙile wani harin da ‘yan bindiga suka suka ƙauyen Zakka da ke ƙaramar hukumar Safana a jihar.

Cikin wata sanarwa da satakaren yaɗa labaran gwamnan, Kaula Mohammed, ya fitar, ya ce tawagar jami’an tsaron ta samu nasara kuɓutar da wani mutum mai shekara 33 da ‘yan bingidar suka kama a lokacin da suka kai harin.

Sanarwar ta ce, da farko gwamnan ya je Safana ne domin ƙaddamar da wani shirin tallafi da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar, Abduljalal Runka, ya shirya a lokacin da ak yi wa jami’an tsaro kiran gaggawa kan harin da ‘yan bindigar suka kai ƙauyen na Zakka.

Bayan samun rahoton ne kuma, sai gwamna ya gaggauta katse taron da yake halarta, inda nan take ya nufi ƙauyen tare da sauran jami’an tsaro.

“Gwamna Radda tare da wasu mambobin tawagarsa sun i sahun jami’an tsaro da suka haɗar da ‘yan sanda da sojojin saman rundunar Hadarin Daji, da na ƙasa, da kuma jami’an tsaron sa-kai da ya ƙaddamar”, in ji sanarwar

An yi arangama da ‘yan bindigar kafin su tsre zuwa cikin tsaunuka.

“Bayan fafatawa mai zafi na tsawon miti 30 da ‘yan bindigar, jami’an tsaron sun samu nasarar kuɓutar da wani mutum mai shekara 33”

Sanarwar ta kara da cewa ‘yan bindigar sun tsere ba tare da kashe wasu daga cikinsu ba.

Bayan daƙile hari ne kuma, Gwamna Radda ya bayar da umarnin gaggauta kai mutumin da aka ƙubutar asibiti bayan da ‘yan bindigar suka harbe shi a ƙafa, in ji sanarwar.

Dama dai gwamnan ya sha yin alwashin shiga daji domin yaƙar ‘yan bindiga a lokutan yaƙin neman zaɓensa.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp