fidelitybank

Gwamnan Kano ya sosa wa wasu Kwamishinoni baya da manjagara tare da yin garambawul

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar da gyare-gyare a majalisar zartarwar jihar, inda ya cire wasu, sannan ya sauya wa wasu ma’aikatu.

A wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar, ya ce gwamnan ya soke ofishin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, wanda Alhaji Shehu Wada Sagagi ke riƙewa, sannan ya sauke sakataren gwamnatin jihar, Dokta Baffa Bichi saboda rashin lafiya.

Sanarwar ta ce gwamnan ya cire kwamishinoni guda biyar: Ibrahim Jibril Fagge na ma’aikatar kuɗi da Ladidi Ibrahim Garko ta ma’aikatar al’adu da yawon buɗe ido da Baba Halilu Dantiye na ma’aikatar watsa labarai da Shehu Aliyu Yammedi na ma’aikatar ayyuka na musamman da Abbas Sani Abbas na ma’aikatar raya karkara.

Sanarwar ta ce gwamnan ya yi sauye-sauyen ne domin inganta aikin gwamnati, da kuma taimaka wa gwamnan wajen kai romon dimokuraɗiyya ga ƴan jihar.

Haka kuma gwamnan ya yi wa wasu kwamishinonin sauyin ma’aikatu, waɗanda suka haɗa da: “mataimakin gwamnan jihar, wanda aka sauya masa ma’aikata daga ƙananan hukumomi zuwa ma’aikatar ilimi mai zurfi, da Mohammad Tajo Usman daga ma’aikatar kimiyya da fasaha zuwa ma’aikatar ƙananan hukumomi, da Dr Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata daga m’aikatar ilimi mai zurfi zuwa kimiyya da fasaha.”

Sauran sun haɗa: “Hajiya Amina Abdullahi daga ma’aikatar jinƙai da rage talauci zuwa ma’aikatar mata, da Nasiru Sule Garo daga ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi zuwa ma’aikatar ayyuka na musamman da Haruna Doguwa daga ma’aikatar ilimi zuwa ma’aikatar albarkatun ruwa.”

Sai dai gwamnan ya buƙaci waɗanda aka cire ɗin su je ofishin gwamna domin a ba su wani aikin daban.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp